Shirin Zabe a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya
December 26, 2025
Za a gudanar da zaben ne a karkashin kulawar Rundunar Wanzar da Zaman Lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya MINUSCA, wadda ta ce za ta samar da tallafin kayan aiki da tsaro, a lokacin zaben da ake ganin zai gudana a bana. Zaben da ke zuwa, bayan yin kwaskwarima a kundin tsarin mulki duk da korafin 'yan adawa.
Ana dai hasashen cewa, Shugaba Faustin-Archange Touadera da ke neman tazarce a karo na uku ne zai samu nasara a zaben shugaban kasa, kasar da ke yanki tsakiyar Afirka da ba ta da iyaka da teku kana daya daga cikin kasahe mafi talauci a duniya da yanayin tsaro ya lafa bayan yakin basasar da aka yi a shekara ta 2010.
Murkushe masu rike da makamai
A cewar masu lura da al'amura da dama, sojoji tare da goyon bayan sojojin haya daga kungiyar Wagner ta Rasha, sun tilasta wa kungiyoyin 'yan tawaye masu dauke da makamai wadanda suka kawo cikas ga zaben da aka yi a karshen shekara ta 2020 ja da baya. Mai shekaru 68 a duniya, Shugaba Touadera da aka zaba a farkon shekara ta 2016 kuma aka sake zabarsa a zagaye na farko na zabe a shekara ta 2020 da a ciki 'yan adawa suka yi zargin magudi, ana ganin har yanzu shi ne zai samu nasara.
'Yan takarar shugaban kasa bakwai ne za su fafata, wadanda daga cikinsu ake ganin biyu ne abokanan hamayyar Touadera wato: Anicet-Georges Dologuélé jagoran ‘yan adawa da ya zo na biyu a wancan zaben da Henri-Marie Dondra, 'yar takarar jamiyyar UNIR kana tsohuwar firaminista. Yanzu haka dai, 'yan adawar suna nuna damuwa a kan zaben, inda suke zargin za a tabka magudi. Gamayyar jam'iyyun adawa ta ma sanar da kauracewa zaben, saboda abin da ta kira rashin gaskiya kamar yadda Anicet Georges Dologuélé jagoran 'yan adawar ya nunar.
Cimma nasarori da samar da ci-gaba?
Shugaba Touadera dai ya kafe ga irin aikin da yayi na samun nasara, wanda a cikin hirarsa da DW shugaban ya ce: "Zuwansa kan karagar mulki an samu ci-gaba a Jamhriyar Afirka ta Tsakiya." A karshen watan Nuwamba, mataimakin sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya kan ayyukan zaman lafiya Jean-Pierre Lacroix da ya kai ziyara a birnin Bangui ya yi furcin cewa: "Yanayin tsaro ya inganta, kana an sami ci-gaba mai mahimmanci a Jamhuriyar ta Afrika ta Tsakiya."