Afirka ta Kudu: Jacob Zuma ya kaurace wa shari'a
July 19, 2019Talla
Wani lauyan da ke kare tsohon shugaban ya bayyana wa hukumar a birnin Johannesburg cewar ba za su ci gaba da ba da hadin kai ba saboda nuna fifiko da hukumar ke yi,da kuma yada ya ce shaidu a gaban hukumar ke tozarta tsohon shugban. Ana dai zargin tsohon shugaban da laifin cin hanci da wani kamfanin na 'yan Indiya na Gupta a zamanin mulkinsa daga shekara ta 2009 zuwa 2018.