1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar da Italiya sun karfafa huldar diflomasiyya

Abdullahi Tanko Bala
January 4, 2018

A wani yunkuri na karfafa dangantakar diflomasiyya kasar Italiya ta yi alkawarin taimaka wa kasar Nijar ta fannin tsaro da kuma yaki da kwararar bakin haure.

https://p.dw.com/p/2qMoM
Mahamadou Issoufou Premierminister von Niger
Hoto: picture alliance/S. Minkoff

Kasar Italiya zata taimaka wa kasar Nijar a fannin tsaro da kwararar bakin haure domin tallafawa kokarin gwamnatin na shawo kian kalubalen da ta ke fuskanta a wadannan fannoni.

Angelino Alfano Innenminister Italien
Ministan harkokin wajen kasar Italiya, Angelino AlfanoHoto: picture-alliance/epa/J. Warnand

Ministan harkokin wajen kasar Italiya, Angelino Alfano ya sanar da hakan yayin kammala ziyarar da ya kai Nijar bayan ganawar da shugabanni da hukumomin kasar.

Ya ce tun a shekarar da ta gabata gwamnatocin kasashen biyu suka kulla yarjeniyoyi wadanda ake fatan zartar da su nan bada jimawa.

Niger  Migranten Flüchtlinge Wüste
Hoto: picture alliance/dpa/D.von Trotha

Abinda ya shafi tsaro a cewar ministan kula da tsaron Nijar Kalla Moutari, babban al‘amari ne.

Yace kasar Italiya z ata taimaka ta fannin tsaro da kayan aiki da suka hada da makamai da kuma horar da dakarun Nijar dabarun yaki da 'yan ta'adda. Ya kiyasata kudin kayayyakin da cewa sun kai CFA miliyan dubu 35

Minsta Kalla ya kuma karyata zargin cewa kasar Italia za ta kawo sojojinta cikin Nijar.

A nata bangaren jakadiyar Nijar a Kasar Italiya Madam Ingade Nana Hadiza Noma kaka, ta ce karfafa hulda tsakanin kasashen biyu wani babban budi ne da Nijar za ta amfana da shi.