1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Isra'ila za ta kori baƙin haure

August 31, 2013

Gwamnatin Isra'ila ta bayyana aniyarta ta aiwatar da shirinta na mayar da wasu baƙin haure na ƙasashen Afirka da ke zaune a ƙasar zuwa wata ƙasa ta gabashin Afirka.

https://p.dw.com/p/19ZWR
An Eritrean holding a banner attends a demonstration against institutionalized racism and new deportation regulations introduced in Israel outside the US Embassy in the southern Mediterranean coastal city of Tel Aviv on June 29, 2012. Israeli Interior Minister Eli Yishai on June 28, gave illegal migrants from Ivory Coast 18 days to leave Israel voluntarily with a cash grant or be forcibly deported without aid. AFP PHOTO/JACK GUEZ (Photo credit should read JACK GUEZ/AFP/GettyImages)
Hoto: Jack Guez/AFP/GettyImages

A lokacin da ya zanta da manema labarai a kan wannan batu ministan cikin gidan isra'ila ya nunar da cewar a watan Oktoba ne za a fara tisa ƙeyar baƙin ba tare da bayyana ƙasar da za ta karɓe su ba. Kimanin baƙin haure dubu hamsin ne waɗanda galibinsu suka fito daga ƙasashen Sudan da sauran ƙasahe ke zauna a Isra'ila.

Gwamnatin Benjamin Netanyahu za ta bai wa duk wanda za a fitar daga ƙasar kimanin Euro dubu da ɗari biyar don su riƙe a hannunsu. Sai dai kuma ta yi barazanar ɗaukan matakan rashin sani da sabo daga bisani kan duk baƙin da za su ci gaba da zama a ƙasar ba bisa ƙa'ida ba.

Mawallafi : Mouhamadou Awal Balarabe
Edita : Abdourahamane Hassane