1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Isra'ila ta saki kuɗaɗen harajin Falasɗinu

March 25, 2013

Gwamnatin ta ba da izinin zuba kuɗaɗen harajin da ta ke cirewa ga al'ummar larabawa mazauna yankunan da ta mamaye zuwa ga hukumar Falasɗinawa.

https://p.dw.com/p/183oo
Israeli Prime Minister Benjamin Netanyahu chairs the Likud-Beiteinu faction meeting at the Knesset (Israel's Parliament) on March 14, 2013 in Jerusalem. Netanyahu is to formally unveil the shape of his long-awaited coalition government which will be sworn in just days before a visit by US President Barack Obama. AFP PHOTO/GALI TIBBON (Photo credit should read GALI TIBBON/AFP/Getty Images)
Hoto: AFP/Getty Images

A cikin wata sanarwa da ofishin fira ministan ta sanar, ta ce an yanke shawarar ne a ƙarshen wani taron majalisar ministocin. A cikin watan Disamba na shekarar bara ne, Isra'ila ta dakatar da shirin, bayan da Majalisar Ɗinkin Duniya ta amince da Falasɗinu a matsayin yar kallo a majalisar.

Sannan ta ummarci ministan kuɗi na ƙasar da ya zuba kuɗaɗen ga hukumar Falasɗinawan. Hakan kuwa na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurika Barack Obama ya kammala wata ziyara a yankin gabas ta tsakiya. Masu yin sharhi a kan al'amura na ganin wannan mataki zai taimaka a samu ƙarin fahimtar juna tsakanin ƙasashen biyu.

Mawallafi : Abdourahamene Hassane
Edita : Saleh Umar Saleh