Tsagaita wuta ta fara aiki a Gaza
November 14, 2019Talla
Wani mai magana da yawun rundunar sojin Israila ya tabbatar da tsagaita wuta tsakanin sojojin da mayakan Jihadil Islami a zirin Gaza a wannan Alhamis bayan shafe tsawon sa'oi 48 ana tashe tashen hankula.
Laftanar kanar Avichy Adraee na runudunar sojin Israilan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter yace duk da haka Israila za ta gasa wa kungiyar 'yan gwagwarmayar Jihadin aya a hannu.
Shi ma ministan harkokin wajen kasar Israel Katz yace sojin Israila za su mayar da martani daidai gwargwado idan aka kai musu hari yana mai cewa Israila ba za ta saurara wa hari daga Gaza ko kuma wani wuri ba.
Kakakin kungiyar Jihadil Islami Musab al Berim shine ya sanar tsagaita wutar wadda kasar Masar ta shiga tsakani