1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

ICC ta zargi Boko Haram da aikata laifukan yaƙi

August 6, 2013

A karon farko tun lokacin da ƙungiyar Boko Haram ta fara kai hare-harenta a Najeriya kotun ƙasa da ƙasa da ke Hague ta zargi kungiyar da kashe farar hula.

https://p.dw.com/p/19L4V
This image taken from video posted by Boko Haram sympathizers shows the leader of the radical Islamist sect Imam Abubakar Shekau made available Wednesday Jan. 10, 2012. The video of Imam Abubakar Shekau cements his leadership in the sect known as Boko Haram. Analysts and diplomats say the sect has fractured over time, with a splinter group responsible for the majority of the assassinations and bombings carried out in its name. (AP Photo) THE ASSOCIATED PRESS CANNOT INDEPENDENTLY VERIFY THE CONTENT, DATE, LOCATION OR AUTHENTICITY OF THIS MATERIAL
Hoto: AP

To an dai daɗe ana samun masu yunƙurin tunkarar kotun ƙasa da ƙasa da ke birnin Hague domin ta bincika abin da ke faruwa a hare-haren da ake kai wa a tsakanin ƙungiyar ta Ahli Sunnah Li Da'awatti Waljihad da martanin da jami'an tsaron Najeriya ke mayar wa, kafin kotun ta ƙasa da ƙasa ta bayana wanan matsayin nata.

Zargin da kotun ƙasa da ƙasa ke yi a kan hare-haren da ƙungiyar ta Ahli Sunnah Li Da'awatti Waljihad ke kai wa a Najeriyar musamman na fararen hula kan cewar ya kai mizanin aikata miyagun laifuffukan yaƙi. Wanda ofishin mai tuhumar aikata miyagun laifuffuka na kotun Fatou Bensouda, ta bayyana cewar bayyanai da suke da su sun nuna alamun hakan abin da ke kama hanyar gudanar da cikakken bincike Barrister Abdulhameed Muhammad ƙwararren lauya ne a fanin dokokin ƙasa da ƙasa don jin illar da ke tattare da hakan.

Nazarin masu yi sharhi a kan wannan al'amari

Ya ce : ‘'Wannan na nuna cewar Najeriyar da al'ummarta sun shiga wani hali kenan a idon duniya saboda irin waɗanan aiyyuka, to amma dai sa'ar da za'a ce Najeriyar na da shi ko kuma wani hanzari shi ne ba ha ka kwai katsam za su shigo ƙasar su gudanar da irin wanan bincike ba. Kuma su waɗanda ake tuhuma ganin suke kamar ba'a ma yi wani hukunci ba, saboda ba wai wata doka ba ce da zata ce ai an kama su an fitar da su Najeriya ko kuma an ɗauki wani mataki. Abubuwan nan yadda suke ta tafiya yana nuna wani hali ne da yanayi da ƙasar ta shiga na maganar ta'addanci''

A residents peers through the shattered widow of a badly-damaged car at the scene of an explosion targeting an open-air beer garden at Enugu Road in the downtown Sabon Gari neighbourhood of the city on July 30, 2013 in Kano. The death toll from a series of bomb blasts that rocked a mainly Christian area of northern Nigeria's largest city of Kano late on July 29 has risen to 12, the military said today, blaming Islamist group Boko Haram for the attacks. The statement blamed the attack on suspected Boko Haram members and said packages that caused the explosions were left in the mainly Christian Sabon Gari area of Kano. AFP PHOTO / AMINU ABUBAKAR (Photo credit should read AMINU ABUBAKAR/AFP/Getty Images) Erstellt am: 30 Jul 2013 Editorial-Bild-Nummer: 175046207 Beschränkungen: Bei kommerzieller Verwendung sowie für verkaufsfördernde Zwecke kontaktieren Sie bitte Ihr lokales Büro. Vollständige redaktionelle Rechte in Großbritannien, USA, Irland, Italien, Spanien, Kanada (außer Quebec). Eingeschränkte redaktionelle Rechte in allen anderen Ländern. Wenden Sie sich bitte an Ihr lokales Büro. Lizenztyp: Lizenzpflichtig Fotograf: AFP/Freier Fotograf Kollektion: AFP Bildnachweis: AFP/Getty Images Max. Dateigröße/ Abmessungen/ dpi: 12,1 MB - 2371 x 1778 Pixel (83,64 x 62,72 cm) - 72 dpi Die Dateigröße für den Download weicht u. U. von den Angaben ab. Quelle: AFP Releaseangaben: Kein Release verfügbar. Weitere Informationen Strichcode: AFP Objektname: Par7627280 Urheberrecht: 2013 AFP Suchbegriffe: Stadt, Zerbrochen, Konflikt, Horizontal, Im Freien, Wohnviertel, Bier, Nigeria, Sehen, Explodieren, Auto, Gewalt, Stadtzentrum, Witwe, Angriff mit Bombe, Eigenheim, Kano - Nigeria, Terrorismus.
Hare-Haren da ƙungiyar ta kai a KanoHoto: AMINU ABUBAKAR/AFP/Getty Images

Hare-haren da ake zargin ƙungiyar na kai wa a kan fararen hula da martanin da jami'an tsaro ke yi tun daga 2009 da yunƙurin kafa gwamnatin islama ya yi dalilin mutuwar mutane fiye da dubu biyu. To ko bayyana cewa sun aikata miyagun laifuffukan yaƙi na iya sauya lamarin ? Malam Abubakar Umar Kari masanin hallayar jama'a ne da ke jami'ar Abuja.

Ya ce ‘'Ba ni tsamani domin ina ganin su magoya bayan wannan ƙungiyar wanan abin baya ma damunsu domin an Don haka ina ganin babu abin da zai canza domin su waɗanan mutane ba su ma amince da wannan tsarin na kotun ba , tasirin da kawai za yi shi ne ya wajen farfaganda kuma mai yiwuwa idan wata rana ƙarfinsu ya ragu aka kama su ana iya gurfanar da su.''

Kotun na zargin ƙungiyar da kashe farar hula

A lokutan baya ƙungiyoyin kare hakin jama'a na Najeriyar da ma ƙasashen duniya sun kasance masu korafin zargin jami'an tsaron Najeriyar da wuce gona da iri suke yi wajen kashe jama'a, a yanzu da kotun ƙasa da ƙasa ba ta yi maganar hukumomin tsaron ba sai na ƙungiyar to ko bayyana wannan mataki da kotun ta yi zai iya sauya yadda wanana ƙalubale ke tafiya a Najeriyar ? Malam Abubakar Umar Kari masanin hallayar jama'a ne da ke jami'ar Abuja.

Im Kampf zwischen der Nigerianischen Armee und Boko Haram in Kano Stadt,hat die Armee heute(30.05.13) diese Munition von Boko Haram entdeckt. Salisu Nasir Zango,Haussa Korrespondent in Kano( Nigeria) hat das Bild geschickt. Foto: Ubale Musa, Haussa / DW
Wasu makaman ƙungiyar Boko Haram da aka kamaHoto: DW/U.Haussa

Ya ce : ''Ni ina ganin wanan fargar jaji ce domin idan har Boko Haram har ta ma aikata wanan laifi, ai kotun yana da wahala ta saka hannu a kansu saboda haka ana ganin Kaman wanan lamarin ne da ke zaman tamkar faɗa amma aikata shi zai yi wuya.''

Duk da kwamitin sulhu da gwamnatin Najeriya ta kafa a ƙokarin shawo kan matsalar har zuwa yanzu lamari na zama wanda ba'a kai ga ganin kama hanyar gano bakin zaren ba, musamman tababar da ke tattare da yunƙurin sulhun kansa .Matsalar rashin tsaro da ke ci gaba da ƙalubalantar arewacin Najeriya tuni ta yi naso tare da shafar ɗaukacin ƙasar.

Daga ƙasa za ku iya sauraron wannan rahoto haɗe da martanin jma'a a kan batun wanda wakilinmu na Gombe Al-Amin ya aiko mana

Mawallafi : Uwais Abubakar Idris

Edita : Abdourahamane Hassane

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani