1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matasa na fuskantar matsar rashin aiki a Ghana

Abdul-raheem Hassan AH
July 6, 2018

A kasar Ghana, harkar man fetur da Gas da bunkaasa a yammacin kasar, sai dai matasa na fuskantar matsalar samun aiki sakamakon rashin kwarewar da ake bukata:

https://p.dw.com/p/30xVk
Ghana Ölplattform vor der Küste
Hoto: Getty Images/AFP/P.U. Ekpei

 Sekondi-Takoradi tagwayen birane ne a kasar Ghana. A gefe guda ruwan kogi ne ke ratsa gine wasu ginen zamani da kuma tsoffin gidaje, can kuma ga jiragen ruwa mallakin kamfanonin mai na shawagi a kan ruwan.Wannan birni dai na cike da tarin arziki, sai dai kawo yanzu 'yan yankin ba su gani a kasa. To my right, wani tudun shakatawa ne da matasa marasa ayyukan yi ke haduwa a kusa da bakin ruwa.Edward Danda Swigam na cikin matasan da ke ganin basa cin wata riba daga masanantun mai da ke yankin. Da irin wannan kosa kosai koyon sanaoin, matasan na fatan kwace damar su ta ayyuka da 'yan ci rani suka mamaye a kamfanonin da ke yankin su. 'Yan ci rani ne da suka iya aiki ne ke samun aiki, amma cibiyar bunakasa ci gaban yammacin kasar ta bullo da tsarin ba wa matasan horo na musamman domin rage zaman kashe wando.