Harin bam ya ruguza ofishin jakadancin Faransa a Libiya
April 23, 2013Gwamnatin kasar Faransa ta yi Allah wadai da harin da aka kaddama akan ofishin jakadancinta da ke birnin Tripoli na kasar Libiya a wannan Talatar. A cikin wata sanarwar da ministan kula da harkokin wajen Faransa Laurent Fabius ya fitar, ya ce Faransa za ta hada gwiwa tare da hukumomin Libiya domin yuin dukkan mai yiwuwa wajen gano musabbabin harin, da kuma wadanda ke da hannu wajen kaddamar da shi.
Tunda farko dai, wani jami'in ofishin jakadancin na Faransa a birnin Tripoli, wanda ya bayyanawa kanfanin dillancin labarai na Reuters batun harin, ya ce suna zaton bam din an dasa shi ne a wata motar da ke kusa da ofishin jakadancin. Ya kuma kara da cewar tarwatsewar ta janyo ta'adi da dama, baya ga masu gadi biyun da suka sami raunin.
Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Usman Shehu Usman