Harin Amirka ya kashe jagoran Kungiyar al-Shabab | Labarai | DW | 07.04.2020
  1. Inhalt
  2. Navigation
  3. Weitere Inhalte
  4. Metanavigation
  5. Suche
  6. Choose from 30 Languages

Labarai

Harin Amirka ya kashe jagoran Kungiyar al-Shabab

Hare-hare ta sama da rundunar sojin Amirka ta kai a Somaliya ne yayi sanadiyar mutuwar jagoran Kungiyar al-Shabab Yusuf Jiis da wasu kusoshin kungiyar biyu.

Babban jami'in rundunar sojin Amirka a Afirka Stephen Townsend,  ya ce, wasu jerin hare-hare biyu da suka kai ta sama ya kashe babban kwamandan kungiyar al-Shabab a Somaliya. Yusuf Jiis da wasu kusoshin kungiyar biyu ne suka rasa rayukansu a farmakin na ranar biyu ga wannan watan na Afrilu inji Janar Townsend.

Amirka ta kwatanta Jiis da ta dadde tana nema ruwa a jallo, da mutum mara imani kuma azzalumi da ke da hannu a kisan fararen hula. Hakazalika ta ce yana adawa da gwamnatin kasar ta hanyar kai hare-hare kan jami'anta da gine-ginenta.

Duk da jan aikin yakar annobar Coronavirus da ke gaban gwamnatin Amirkan, ta ce ba zata sassauta matakinta na yakar Al-shabab ba. Kungiyar dai, na da alaka da kungiyar al-Qaeda, ta kuma kwashi shekaru tana kai hare-hare a Somaliya inda ta take da karfin iko da kasashen da ke makwabtaka da ita.