1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojan Faransa sun kashe wani jigo a kungiyar 'yan ta'adda

Abdoulaye Mamane Amadou
November 6, 2019

Rundunar tsaron Faransa ta bayyana kisan daya daga cikin jiga-jigan kungiyoyin jihadin a yayin wani sumame da rundunar tsaron kasar Faransa ta ta kaddamar a Mali a farkon watan jiya.

https://p.dw.com/p/3SWw4
Mali islamistische MUJWA Rebellen in Gao Konvoi mit Außenminister von Burkina Faso
Hoto: Reuters

Ministar tsaron kasar ta Faransa ta tabbatar da kisan shugaban kungiyar ta Jama'at Nusrat al-Islam wal-Muslimin a shafinta na Twitter, inda ta ce an halakashi ne tun a ranar tara ga watan jiya. Ali Maychou na daya daga cikin shugabannin kungiyoyin addini masu kaifin kishin Islama a Mali, Faransa na zargin Ali Maychou ne da hannu wajen kaddamar da hare-haren ta'addanci ga dakarun kasar da na Amirka har da na rundunar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya da ke aikin tabbatar da tsaro a Mali.