1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Habasha: Mata sun samu kashi 50 na mukamai

Zulaiha Abubakar
October 16, 2018

Firaministan kasar Habasha Abiy Ahmed ya bayar da kaso 50 cikin dari na mukaman ministocin gwamnatin kasar ga mata bayan amincewar majalisar dokokin kasar.

https://p.dw.com/p/36d9p
Addis Abeba, Äthiopien, Äthiopischer Premierminister Abiy Ahmed im Parlament
Hoto: DW/Y.Geberegziabher

Tun kafin mika bukatar sa ga zauren majalisar, sabon Firaministan mai shekaru 42 ya bayyana cewar yana fatan mata za su yi amfani da wannan tagomashi wajen nunawa al'ummar kasar cewar za su iya shugabanci fiye da maza. Daga cikin matan da aka nada a mukamansun hada da Aisha Muhammad Musa wacce ta samu mukamin ministar tsaro a karon farko a kasar.

Yanzu dai majalisar ministocin ta kunshi mutane 20 ne kachal maimakon 28 din da ta kasance a baya.