1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Heiko Mass zai je Tsibirin Madeira

Abdourahamane Hassane
April 18, 2019

Fadar gwamnatin Jamus ta sanar da cewar ministan harkokin waje na Jamus Heiko Masa zai isa a tsibirin Madeira na Portugal, inda wasu Jamusawa 29 suka rasa rayukan a sanadiyyar hadarin motar bas.

https://p.dw.com/p/3H1r1
Portugal Busunglück auf Madeira
Hoto: Getty Images/AFP/R. Silva

Helge Braun darakta a fadar gwamnatin ta Angela Merkel ya ce ministan na harkokin waje na Jamus Heiko Maas  zai je tsibirin na Madeira domin ganin halin da ake ciKI. Zai kuma tafi ne tare a rakiyar likitoci domin ba da kulawa ta musammun ta kiwon lafiya ga wadanda suka raunana a sakamakon hadarin. Motar bas din wacce ke dauke da Jamusawa 49 maza da mata 'yan yawan shekatawa masu shekaru 40 zuwa 60 ta kife da su bayan da matukin motar ya saki daben da yake kansa.