1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwajin kwakwalwa ga maharin Christchurch

Ahmed Salisu
April 5, 2019

Kotu a New Zealand ta bada umarnin yin gwajin kwakwalwa ga mutumin nan da ake zargi da hallaka mutane 50 tare da jikkata wasu da dama a wasu masallatai biyu da ke birnin Christchurch a kudancin kasar.

https://p.dw.com/p/3GMFZ
Neuseeland | Anschlag von Christchurch | Brenton Tarrant
Hoto: Reuters/M. Mitchell

A wani zama da kotun ta yi a wannan Juma'ar, mai shari'a Cameron Mander ya ce wasu kwararru za su duba kana su tantance ko Brenton Tarrant na da cikakken hankalin da zai iya fuskantar shari'a.

Yayin zaman kotun na yau, Brenton mai shekaru 28 da haihuwa, wanda dan asalin kasar Austreliya ne ya gurfana gaban alkalin ne ta faifan bidiyon da aka haska kai tsaye daga gidan yarin da ake tsare da shi a birnin Auckland.

Mutanen da suka jikkata da kuma 'yan uwan wadanda suka rasu a harin na 15 ga watan Maris da dama ne dai suka halarci zaman kotun a birnin na Christchurch.