1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

MDD: Guterres zai yi Karamar Sallah a Afirka

April 30, 2022

A yayin ziyarar tasa, Guterres, zai yi buda baki da Shugaban Senegal Macky Sall sannan zai gana da Shugaba Mohamed Bazoum na Nijar da kuma Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya.

https://p.dw.com/p/4AeOg
Äthiopien Gipfeltreffen der Afrikanischen Union in Addis Abeba Antonio Guterres
Hoto: Getty Images/AFP/S. Maina

Sakatare Janar na MDD, Antonio Guterres, ya shirya kawo ziyara a kasashen Afirka ta Yamma domin yin shagulgulan Karamar Sallah da mabiya addinin Islama albarkacin kammala azumin watan Ramadan.

Sanarwar da MDD ta fitar ta nuna cewa Guterres zai isa kasar Senegal a wannan Asabar. A ranar Litinin kuma zai je Jamhuriyar Nijar, sai kuma Najeriya da sakatare janar din zai ziyarta a ranar Talata kafin ya koma ofishinsa da ke Amurka.

Ziyarar ta  Guterres za ta ba shi damar ganawa da kungiyoyin sa kai da na addinai da kuma iyalan mutanen da rikici ya tagayyara a kasashen Sahel, inda zai duba yadda zuwan coronavirus da sauyin yanayi suka shafi rayuwar marasa galihu.