1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gudumawar APC ga inganta dimokradiyyar Najeriya

August 12, 2013

Janar Buhari ya ce burin samar da jam'iyyar APC shi ne kyautata rayuwar 'yan Najeriya.

https://p.dw.com/p/19OHA
Muhammadu Buhari from the opposition party ANPP (All Nigeria People's Party) acknowledges support after voting in Daura, Nigeria, Saturday, April. 19, 2003. President Olusegun Obasanjo seeks a second term in elections Saturday that pose the stiffest test for Nigeria's young democracy since his election four years ago ended 15 years of military rule. (AP Photo/Schalk Van Zuydam)
Hoto: AP

Tsohon shugaban mulkin sojan Najeriya janar Muhammadu Buhari mai ritaya, ya nuna alamun tsayawa takara a zaben 2015 idan gamayyar jam'iyyun adawa ta APC ta bukace shi da yin haka. Cikin wata hira da ya yi da wakiliyarmu ta Jigawa Zainab Shuaibu Rabo Ringim, janar Buahri ya yi alkawarin kyautata halin rayuwar 'yan Najeriya idan hakarsa ta cimma ruwa a zabe na gaba.

Janar Buhari, ya kuma bayyana cewar, za su dauki dukkan matakan da suka wajaba domin hana sojan gona karbe akalar tafiyar da harkokin jam'iyyar, tunda kuwa a cewarsa, sun koyi darussa da dama daga zabukan da suka gabata.

Mawallafiya : Zainab Shuaibu Rabo
Edita           : Saleh Umar Saleh