1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Goyon bayan Jamus ga matakan Faransa a Mali

January 14, 2013

Jamus tace zata baiwa Faransa duk gudummuwar da take bukata game da rikicin Mali amma ba zata tura sojojinta su shiga yaki a can ba.

https://p.dw.com/p/17Jjf
Hoto: Reuters

Gwamnatin Jamus tana goyon baya da taimakon  matakan soja da Faransa take dauka kan yan tawaye musulmi a kasar Mali,  kuma tace tana nazari a game da yiwuwar  baiwa Faransa  din karin gudummuwar kayan yaki. To amma a wani bayani da gwamnati ta gabatar a Berlin, tace  Jamus ba zata tura sojoji su shiga yakin dake gudana a kasar ta Mali ba.

Ba kamar a lokacin da rundunar  kasa da kasa da tayi yaki a Libya a watan Maris na shekara ta 2011 ba, inda Jamus ta zama saniyar ware, a wannan karo gwamnati a Berlin ta fito fili ta baiyana cikakken goyon bayanta ga matakan soja da Faransa take dauka a Mali. Gwamnatin tace Faransa tana daukar matakai  da suka dace kuma suka kamata a dauke su, wadanda burinsu shine a dakatar da kusantar da  mayakan yan tawayen Mali suke yi  ga babban birnin kasar Bamako. Ministan tsaron Jamus,   Thomas de Maiziere yace tun da farko sai da Faransa ta sanarwa Jamus shirin ta, kuma Faransa din tana da cikakken goyon baya daga garemu. Shima ministan harkokin waje, Guido Westerwelle yace Turawa suna da matukar sha'awar ganin kasar ta Mali bata zama  maboya kuma dandalin  aiyukan yan tarzoma a yankin da ga baki ga hanci yake tsakanin sa da Turai ba. Gwamnati a Paris, inji bayani na Jamus, tana tafiyar da aiyukanta ne bisa dacewa da bukatun kudirin kwamitin sulhu na majalisar dinkion duniya. Ana kuma tattaunawa da Faransa  game da fannonin da Jamus zata iya baiwa kasar taimako. kamar yadda kakakin ma'aikatar  harkokin waje,  Andreas Peschke ya nunar:

Yace irin wannan taimako alal misali, yana iya kasancewa ta hanyar  baiwa Faransa kayaiyaki ne da take bukata  a matakan na soja a Mali, ko taimakonta a fannin aiyukan likitoci da magunguna ko taimakon jin-kai. Wadannan sune abubuwan da musmaan aka cimma daidaitawa kansu.

Merkel PK beim EU Gipfel in Brüssel
Shugabar gwamnatin Jamus Angela MerkelHoto: Reuters

To sai dai Jamus tace ba zata tura sojojinta su shiga yakin na Mali ba. Wannan kuwa mataki ne dake samun goyon baya  har ma daga  yan adawa a kasar ta Jamus, inda Jamus din tace wannan ra'ayi nata ya dace gaba daya da ra'ayin kungiyar hadin kan Turai. Kakakin  gwamnatin taraiya, Steffen Seibert dake bayanin wannan matsayi na Jamus  yace:

Sakamakon hadin kai na al'ada da dangantaka da kuma tarihin dake tsakanin Faransa da wannan yanki na nahiyar Afrika, uma musmman ganin cewar Faransa yanzu haka tana da rundunonin sojan ta da ta tsugunar dasu  a wasu kasashe makwabtan Mali, Faransa din  tana da huldodi na musamman, kuma tana da isassun sojoji a kusa  da zasu iya tafiyar da wannan aiki. 

Kakakin na gwmanatin yace wannan ma shi ya sanya  Mali ta gabatar da rokon nata na tgaimako ne zuwa ga Faransa amma ba zuwa ga Jamus ba. Gwamnati a Berlin  inji  ministan tsaro Thomas de Maiziere, tana ma da ra'ayin cewar  kamata yayi a gagauta baiwa  matakan kawar da yan tawayen da suka mamaye arewacin Mali wata fuska ta yan Afirka. Saboda haka ne Jamus zata taimakawa kokarin soja da na siyasa  da kungiyar  ECOWAS ta kasashen Afirka ta yamma take yi kan rikicin na Mali. Yanzu haka dai ana ci gaba da rade-radi a game da irin taimakon da kungiyar ta ECOWAS zata nema daga Jamus, saboda ranar Laraba  ake sa ran isar  shugaban  Cote d'Ivoire Alassane Ouattara a Berlin  domin ziyarar da  tuni aka shirya yinta. Ouattara shine shugaban ECOWAS a yanzu, kuma ana  zaton zai yi amfani da tattaunawarsa da shugaban gwamnati, Angela Merkel domin gabatarwa Jamus rokon kungiyar. Jamus dai tuni ta baiyana   shirin ta bada gudummuwa a rundunar da zata kunshi  mutane 200 da za'a tura domin horad da sojojin Mali, bisa manufar karfafa  zaman lafiya a kasar.

Ansar Dine Kämpfer in Mali
Mayakan kungiyar yan tawaye ta Ansar Dine a arewacin MaliHoto: Romaric Ollo Hien/AFP/GettyImages

Mawallafi: Bernd Gräßler/Umaru Aliyu
Edita: Usman Shehu Usman

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani

Nuna karin labarai