Ghana: Gwamnati ta nemi afuwar 'yan kasa
November 18, 2022Talla
Ministan ya nemi afuwar 'yan kasar ce a lokacin da ya bayyana gaban wani kwamiti na majalisar dokokin kasar da ke gudanar da bincike a kansa da kuma irin aikin da ya gudanarwa.
Kasar ta Ghana dai a dan tsakanin nan ta fada cikin masassarar tattalin arziki inda farashin kayayyaki musamman ma na masarufi ya yi tashin gwaron zabi, lamarin da ya sanya 'yan kasar kokawa har ma suka nemi da a sallami ministan daga bakin aikin yayin da wasu 'yan kasar ke neman gwamnatin Shugaba Nana Akuffo Ado ta yi murubus.