1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

G5 Sahel: Fito na fito da ta'addanci

Abdoulaye Mamane Amadou
December 16, 2019

Shugabannin kasashen kungiyar G5 Sahel sun bayyana matakin kara karfafa huldarsu da kasashen waje domin kawar da aiyukan ta'addanci da ke ci gaba da addabar kasashen biyar.

https://p.dw.com/p/3UsJG
Mauretanien Frankreich Afrikanische Union
Mun yi amfani da tsohon hoton shugabannin kasashenHoto: picture-alliance/L.Marin

A yayin wani babban taron kolinsu da suka kammala a birnin Yamai a yammacin jiya Lahadi (15-12-2019) Shugabannin sun bukaci tallafin kasashen na waje tare da kaddamar da wani gagarumin shiri kan nan zuwa shekaru biyu masu zuwa na kakkabe mayakan jihadin da suka samu gindin zama a yankunan kasashen Burkina Faso Mali da Jamhuriyar Nijar, a cewar sanarwarsu ta bayan taron.

taron na shugabannin na zuwa ne kwanaki bayan wani mumunan harin ta'addancin da ya afkawa sojan Jamhuriyar Nijar a garin Inates, da kuma ya hallaka sojan fiye da 70.