F.W.de Klerk ya rasu sakamakon ciwon daji
November 11, 2021Talla
De Klerk ya jagoranci Afirka ta kudu a karshen wa'adin mulkin wariya kafin daga bisani marigayi Nelson Mandela ya zama shugaba a 1994. De Klerk ya karbi lambar yabo ta zaman lafiya ta Nobel tare da Nelson Mandela wanda suka yi aiki tare wajen kawo karshen wariyar launin fata a Afirka ta Kudu. Ya rasu sakamakon cutar cancer bayan ya sha fama da jinya.
Wani mai magana da yawun gidauniyar F.W.De Klerk ya tabbatar da rasuwarsa a wannan Alhamis 11.11.2021). FW De Kler ya yi kaurin suna a Afirka ta Kudu inda mutane da dama suka zarge shi da kuntata wa bakar fata 'yan Afirka ta Kudu da masu fafatukar yaki da wariyar launin fata a zamanin mulkinsa.