1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Firaministan kasar Jordan ya sauka daga mulki

Zulaiha Abubakar MNA
June 4, 2018

Firaministan ya bayyana daukar wannan mataki ne don dakile rikicin da kasar ta shiga a kan wasu sabbin sharuddan inganta tattalin arziki a yayin ganawarsa da Sarki Abdullahi Ibn Al-Hussein a wannan Litinin.

https://p.dw.com/p/2yubK
Jordanien Hani Mulki
Hoto: Imago

A baya dai matakan tsuke bakin aljihun da Firaministan kasar Hani Al-Mulki ya dauka don samarwa kasar ta Jordan karin kudin shiga, wadanda suka hada da rage kudin tallafin gwamnati a kan wasu muhimman kayan masarufi da suka hada da biredi a fadin kasar, na daga cikin abubuwan da suka jawo masa bakin jini, lamarin da ya haifar da  wata zanga-zanga irinta ta farko a kasar.

Al'umma kasar sun bayyana kin jinin karin kudin haraji tare kuma da kiran tsohon Firaminista a kan ya sauka daga mulki sakamakon zarginsa da suka yi da gazawa wajen shugabanci.

Shirye-shirye sun yi nisa don kaddamar da sabuwar gwamnati a kasar kamar yadda Sarki Abdullah Al-Hussein ya bada umarni.