1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fafutukar warware rikicin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

October 20, 2013

Shugabannin da gwamnatoci na ƙasashen yankin tsakiyar nahiyar Afirka na ƙungiyar za su gudanar da wani taro a Cadi domin samar da mafita ga rikicin ƙasar.

https://p.dw.com/p/1A2tS
Chief of the SELEKA rebel alliance Michel Djotodia sits on January 17, 2013 in Bangui during a ceremony. Opposition figure Nicolas Tiangaye was officially appointed today Prime Minister of the Central African Republic's new national unity government, President Francois Bozize said after a ceremony in the capital Bangui. The announcement was in line with a peace deal struck between the ruling party, the Seleka rebels and the democratic opposition in the Gabonese capital of Libreville last week.
Hoto: Getty Images

Taron wanda shugaban ƙungiyar ne da ke ci yanzu Idriss Deby ya kira shi, zai tattauna matsalar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya,wacce ke fama da tashin hankali na ƙabilanci da kuma hare-hare da fyaɗe da sojoji ke kai wa akan farar hula.

Wannan taro dai shi ne na biyar da ƙungiyar ta ke yi a kan Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya,tun bayan juyin mulkin da Michel Djotodia ya yi wa shugaba Francois Bozize,a cikin watan Maris da ya wuce a ƙarkashin jagorancin ƙungiyar 'yan tawayen ta SELEKA. A cikin watan jiya shugaba Francois Hollande na Faransa, ya ce zai ƙara yawan sojojinsa a Jamhuriyar Afirka ta Tasakiyar,domin kawo ɗauki ga rundunar tsaro ta ƙasashen Afirka MISCA don samar da zaman lafiya.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane.
Edita : Zainab Mohammed Abubakar