Fafutukar warware rikicin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya
October 20, 2013Taron wanda shugaban ƙungiyar ne da ke ci yanzu Idriss Deby ya kira shi, zai tattauna matsalar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya,wacce ke fama da tashin hankali na ƙabilanci da kuma hare-hare da fyaɗe da sojoji ke kai wa akan farar hula.
Wannan taro dai shi ne na biyar da ƙungiyar ta ke yi a kan Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya,tun bayan juyin mulkin da Michel Djotodia ya yi wa shugaba Francois Bozize,a cikin watan Maris da ya wuce a ƙarkashin jagorancin ƙungiyar 'yan tawayen ta SELEKA. A cikin watan jiya shugaba Francois Hollande na Faransa, ya ce zai ƙara yawan sojojinsa a Jamhuriyar Afirka ta Tasakiyar,domin kawo ɗauki ga rundunar tsaro ta ƙasashen Afirka MISCA don samar da zaman lafiya.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane.
Edita : Zainab Mohammed Abubakar