1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An koma gwabza yaki a arewacin Kamaru

Abdourahamane Hassane
December 10, 2019

Yaki ya sake barkewa a yankin arewa maso yammacin Kamaru tsakanin dakarun gwamnati da na 'yan aware na Ambazoniya masu fafutukar kafa kasarsu.

https://p.dw.com/p/3UZ8o
Kamerun Symbolbild Soldaten im Norden ARCHIV
Hoto: Getty Images/AFP/R. Kaze

Kungiyoyin da ke yin aikin agaji a yankin sun ce farar hula sun fada cikin tarkon sasan biyu masu gaba da juna, lamarin ya kara dagulewa ne bayan da taron kasa da shugaba Paul Biya ya kira don tattaunawa ya gaza cimma wani sulhu tsakanin gwamatin da 'yan aware. Kungiyar agaji ta Human Rights Watch ta ce daga watan Yuli zuwa yau kusan farar hula 130 a ka kashe a tashin hankalin da a shekaru biyu sama da mutane dubu 700 suka fice daga matsugunansu.