SiyasaJamus
MDD: Ana samu barazanar karancin abinci
November 8, 2021Talla
Cikin wata sanarwa da ta fitar a birnin Roma na Italiya, Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce kimanin mutum miliyan 45 ne ke fuskantar barazanar karancin cimaka a bana, kana galibin wadanda suka kara adadin alkaluman sun fito ne daga kasar Afghanistan.
Annobar corona ma dai na daga cikin wasu dalilai da suka kara ta'azzara barazanar da duniya ke fuskanta a wannan shekara, a cewar babban daraktan hukumar David Beasley a yayin da yake zantawa da manaima labarai.