Muna amfani da "Cookies" domin inganta abubuwan da muke wallafawa a intanet. Za ku iya samun karin bayani a kundin kare bayananmu.
A cikin shirin za a ji shirye-shiye kamar haka: Ji ka karu, Zabi sonka da Ra'ayin Malamai
A cikin shirin za a ji cewa mahara sun kashe 'yan gudun hijirar Mali da ke samun mafaka a yankin Tahoua na Jamhuriyar Nijar mai iyaka da Mali.
A cikin shirin za a ji wasu muhimman batutuwan da suka dauki hankali a nahiyar Afirka a wannan makon mai karewa
A cikin shirin za a ji cewa a Najeriya mahukunta da kungiyoyin fararen hula sun dauki matakan kaucewa rigingimun a lokacin zabe, a Nijar gwamnati ta dauki doka da za ta bai wa sojojin kasar da iyallansu damar daukar nauyin kiwon lafiyarsu.
Shirin Gaskiyar Magana na wannan makon ya duba yadda yakin neman zabe ke tafiya a Najeriya, a yayin da ya rage kasa da wata guda al'ummar kasar su tafi rumfunan zabe. Mun gayyato Ladan Salihu na jam'iyyar PDP da Buba Galadima na jam'iyyar NNPP.
Yayin da Shugaban darikar Katolika na duniya ke shirin fara ziyara a Sudan ta Kudu a wannan Jumma'a, da dama daga cikin 'yan kasar na fatan ganin Paparoma Francis ya kawo sauyi ga tashin hankali da fagen siyasar kasar ya saba fuskanta.
A cikin shirin za a ji cewa a Najeriya, 'yan kasar na nuna fargaba kan tsaro yayin zabukan da za a gudanar a kasar, bisa la'akari da lamuran da suka fari yayin gangamin yakin neman zabe. A Jamhuriyar Nijar kuwa, mata ne suka tashi haikan wajen samar da gishiri da kuma kanwa domin dogaro da kai.
A cikin shirin za a ji martanin al'ummar Ghana kan karin kudin wutar lantarki da na ruwa, a Najeriya kungiyoyin matasa sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan takarar neman shugaban kasa.
Shirin ya kunshi labarai da rahotanni har da rikicin siyasar jam'iyyar APC mai mulki a tarayyar Najeriya.
A shirinmu za ku je cewar Paparoma Francis na maida hankali kan lamuran coci da ke taka muhimmiyar rawa a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango mai fama da tashe tashen hankula. Idan ya tashi kwango, zai je Sudan ta Kudu.
A cikin shirin za a ji a Najeriya yayin da ya rage kasa da makonni 4 a kai ga babban zaben kasar, hankalin miliyoyi al'umma na kara karkata zuwa ga fasahar BVAS wacce za a yi amfani da ita a kokarin neman tabbatar da ingantaccen zabe.
Hankalin miliyoyin 'yan Najeriya ya karkata zuwa amfani da fasahar BVAS a kokarin tabbatar da ingantaccen zaben 2023.
Sabon tsarin babban bankin Najeriya na sauya takardun kudi ya jefa jama'a da dama cikin zullumi duk da karin wa'adin da bankin na CBN ya yi.
A cikin shirin za a ji yadda ta kaya a jamhuriyar Nijar bayan da wani Kamfanin Aikin Hajj da Umara ya maka Hukumar da ke kula da wannan fanni a Kasar COHO a katu, a Najeriya al'umma na ci gaba da jimamin rasuwar Sarkin Dutse Mai martaba Dr. Nuhu Muhammad Sunusi.
Za a ji martanin 'yan Nijar bayan Aljariya ta lallasata da ci 5 -0 a gasar CHAN
Gwamnan babban bankin Najeriya Godwin Emefiele ya bayyana a gaban kwamitin majalisar wakilan kasar inda ya amince da sabbin matakai na bada dama ga ‘yan kasar su mayar da tsofafin takardar kudi na Naira.
A cikin shirin za a ji cewa duk da karin wa'adin da babban bankin Najeriya ya yi na maida tsofaffin kudi, al'ummar jihar Bauchi na fuskantar karancin sababbi da tsofaffin kudin domin gudanar da harkokinsu na yau da kullum.
Chernor Bah na cikin masu kamfanin Purposeful, matashin ya zagaya duniya. Kungiyarsa mai cibiya a Saliyo, na aiki a kasashe sama da 90 da nufin karfafa wa mata gwiwa a duniya.
A cikin shirin za a ji cewa, shugabannin kungiyoyi na ci gaba da yin Allah wadai da harin da ya hallaka wasu Fulani makiyaya kimanin 40 a jihar Nassarawan Najeriya. A Nijar an bude babba taron kasa karo na farko kan shirya aikin hajji da Umara, domin bitar matsalolin da ke kawo cikas ga tafiyar da aikin hajji a kasar.
A cikin za shirin a ji yadda shugaba Buhari ya kai ziyrar kaddamar da ayyuka a Kano, a Nijar an buda babban taron kasa kan shirya aikin Hajji da Umara.