1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

matakin 'yan gudun hijira na shiga Amirka

Salissou Boukari
November 10, 2018

Dubban 'yan gudun hijira na yankin Latin Amirka sun ci gaba da tafiyar da suke yi a kafa da zimmar shiga Amirka duk da matakin Shugaba Donald Trump na kasar ta Amirka kan matakan hana 'yan gudun hijira shiga.

https://p.dw.com/p/381ww
Migration Venezuela USA Flüchtlinge
Hoto: Reuters/A. Latif

Rahotanni daga kasar Mexiko na cewa ayyarin mutane kimanin dubu biyar 'yan gudun hijira masu burin shiga kasar Amirka ko ta halin kaka, sun dauki hanyarsu a wannan Asabar inda suke tafiya a kafa duk kuwa da tarin gajiya da ma rashin lafiya.

Tun dai a ranar Alhamis 'yan gudun hijiran sun nemi hukumar Majalisar Dinkin Duniya mai kula da 'yan gudun hijira ta ba su taimakon motocin safa har 150 domin su kara gaba, sai dai ganin hakarsu ba ta cimma ruwa ba, ayyarin masu neman shiga kasar ta Amirka sun ci gaba da tafiya a kafa.

Tun dai daga ranar 13 ga watan Oktoba ne ayarin mutanen ya bar birnin San Pedro Sula na kasar Honduras a wani mataki na gujewa matsalar talauci da tashe-tashen hankulla da suka yi musu katutu da zimmar zuwa kasar Amirka. Sai dai shugaban kasar ta Amirka Donald Trump ya danganta wannan mataki a matsayin mamaya.