1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

David Cameron ya nemi Scotland ta zauna cikin Birtaniyya

Mohammad Nasiru AwalSeptember 10, 2014

Firaministan Birtaniyya ya kai ziyarar neman goyon baya a yankinn Scotland gabanin kuri'ar raba gardama a ranar 18 ga watan Satumba.

https://p.dw.com/p/1D9t4
Ed Miliband, Nick Clegg, David Cameron
Hoto: Getty Images/L. Pitarakis

Mako guda gabanin kuri'ar raba gardama game da 'yancin kan yankin Scotland, Firaministan Birtaniyya David Cameron ya yi kira da ci gaba da zaman Daular Birtaniyya a matsayin kasa daya al'umma daya. Ya fadi haka ne a birnin Erdinburgh inda ya kara da cewa Birtaniyya wani iyali ne na kasashe wadda kuma tun shekaru 300 da suka wuce yankin Scotland ke cikinta don radin kai. Cameron da mataimakinsa kuma dan jam'iyyar Liberal Democrat Nick Clegg da jagoran 'yan adawa na Labour Ed Miliband suna yankin a kokarin shawo kan masu kada kuri'a na Scotland su amince da zama cikin kasar Birtaniyya. A ranar 18 ga watan nan na Satumba 'yan Scotland za su yi zabe raba gardama game a ballewar yankinsu daga Birtaniyya. Kuri'ar jin ra'ayin jama'a ta nuna cewa ana kafada da kafada tsakanin masu adawa da masu goyon bayan samun 'yancin kan.