1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Lafiya

Cutar Ebola ta kashe mutane 17 Kwango

Suleiman Babayo
May 8, 2018

Bincike ya tabbatar da cewa cutar Ebola ta bulla a yankin arewa maso yammacin Jamhuriyar Demokaradiyyar Kwango inda mutane 17 suka mutu.

https://p.dw.com/p/2xNi2
Ebola virus
Hoto: picture alliance/dpa/EPA/Frederick A. Murphy

Jami'ai a Jamhuriyar Demokaradiyyar Kwango sun tabbatar da cewa kimanin mutane 17 suka hallaka sakamakon cutar Ebola da ta bulla a kasar.

Mahukunta sun ce cutar ta bulla cikin yankin arewa maso yammacin kasar. Tun a makon jiya ranar 3 ga wannan wata na Mayu aka samu rahoton bullar cutar inda kimanin mutane 21 suka kamu da zazzabi daga ciki 17 suka rasu. Sakamakon da aka samu a cibiyar bincike da ke birnin Kinshasa ya tabbatar da cewa biyu daga cikin mutanen sun kamu da cutar Ebola.