Mali: Cisse ya yi fatali da sakamakon zabe
August 13, 2018Talla
Jagoran adawa a kasar Mali Soumaila Cisse ya bayyana a wannan Litinin cewa zai yi fatali da sakamakon zabe zagaye na biyu da aka yi a kasar wanda ya ce cike yake da magudi, ya kuma yi kira ga al'ummar kasar "da su tashi tsaye".
Ya ce sun tabbatar da aikata magudi a zaben don haka ba za su amince da sakamakon ba. Cisse ya bayyana haka ne ga taron manema labarai a hedikwatar jam'iyyarsa da ke birnin Bamako.
Ya ce al'ummar Mali ba za su lamunci murdiyar zabe ta masu mulkin kama karya ba.