1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Cin hanci ya samu gidin zama a kan sha'anin ilimi a Afirka

November 21, 2013

A cikin rahoton da ta bayyana Kungiyar Transparency International da ke yaƙi da cin hanci da rashawa a duniya ta ce lamarin ya yi ƙamari a cikin makarantu a nahiyar.

https://p.dw.com/p/1AMA6
Entwicklungshilfe in Afrika - Bildung ARCHIV - Ein Junge schreibt während des Unterrichts in einer Schule im nigerianischen Dorf Tibiri auf der Tafel (Archivfoto vom 05.11.2007, Illustration zum Thema Entwicklungshilfe). Wenn es um Bildungsprogramme und Gesundheitsprojekte, Brunnenbau oder Dürrebekämpfung in den Entwicklungsländern in Afrika, Asien und Lateinamerika geht, wollen die Betroffenen stärker als bisher mitreden. Das wurde auf der am Donnerstag (04.09.2008) endenden dreitägigen internationalen Konferenz über effektivere Entwicklungshilfe in Accra deutlich. Auch internationale Hilfsorganisationen sprachen sich dafür aus, die Verantwortung der Länder der Dritten Welt zu stärken. Foto: Thomas Schulze (zu dpa-Korr. "Ringen um die Entwicklung - Zivilgesellschaft pocht auf Mitsprache" vom 04.09.2008) +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

Kama daga cinikin na takardun shaida ya zuwa na satar jarrabawa dama na lalata da dalibai dai sannu a hankali dai harkokin ilimi na samun komawa baya a ɗaukacin nahiyar baki ɗaya.

Rahoton ya ambato ƙasashe da dama irinsu Najeriya da Nijar

Rahoton mai shafuka sama da 400 dai ya taɓo matsalolin kama daga na saida takardun jarabawa a jamhuriyar Nijar ya zuwa sace kuɗaɗen kasafin kuɗin ilimi a ƙasar Kenya da kuma ƙaurace war malaman Makaranta a Jamhuriyar Kamaru sannan kuma da uwa uba lalata da ɗalibai 'yan makaranta a Tarrayar Najeriya.Sabon rahoton da ke zaman irin sa na farko da ke nazarin batun na cin hanci a cikin harkar ilimi dai alal misali ya ambato ƙasashen Ghana da Kamaru da Tarrayar Najeriya a matsayin na kan gaba cikin ƙasashen da ɗalibai kan ba da na goro domin samun ilimi a duniya baki ɗaya.Sabon rahoton dai a faɗar Marie- Angie Kalenga da ke zaman babbar jami'ar ƙungiyar da ke kula da yankin yammacin Africa dai na ƙara tada hankali da nuna jan aikin dA ke a gaba a ƙoƙarin nahiyar na wadatar da ilimin al'ummarta.Ta ce:''Rahoton na nuna babu wani sashen na ilimi a nahiyar da ya tsira daga batu na cin hanci .Ko dai a mataki na firamare.''

In ländlichen Gebieten bilden Familie und Dorfgemeinschaft bedeutende soziale Netzwerke. Industrialisierung und Urbanisierung lösen diese Strukturen indes auf. Eine fundierte Schulbildung ist oft das Sprungbrett in eine selbstbestimmte Zukunft. Die Alphabetisierungsrate in Nigeria liegt bei 68%. Ein kürzlich veröffentlichter UNESCO-Bericht beklagt: über 4 Millionen Mädchen haben keinen Zugang zu Grundschulbildung. Eingestellt am 10.12.2010. Foto: Stefanie Duckstein
'Yan makaranta a NajeriyaHoto: DW/Stefanie Duckstein

Shin yaya lamarin yake a Najeriya dangane da rahoton ?

A nan Najeriya da ke masauƙin baƙi dai rahoton na zuwa ne a daidai lokacin da jami'oin ƙasar ke cikin wattanni na biyar ba darasi, a wani abun da ke nuna alamun rushewar tsarin da ƙasar ke dogaro da shi da nufin tabbatar da ci gaban al'ummarta.Tuni dai dama ilimi a mataki na sakandare ya koma na kuɗi inda iyaye kan zaɓi makarantu na kuɗi masu ɗan karen tsada domin tabbatar da samar da cikaken ilimi a cikin ya'yansu.Duk da cewar an kai ga ƙaddamar da makarantun almajirai har ya zuwa yanzu ƙasar ta Najeriya ce ke ta kan gaba ga batun yara ƙanana da basu karatu inda aka tsara sama da yara miliyan 10 na yawo a tituna babu karatu.

HANDOUT - Mädchen in Niger, die sich freuen, eine Schule besuchen zu dürfen, halten kleine Tafeln, auf denen «11. Oktober» geschrieben steht, in ihrem Klassenzimmer hoch (undatiertes Foto). Die internationale Hilfsorganisation «Plan» hat die Vereinten Nationen davon überzeugt, dass die Welt auch einen Weltmädchentag braucht. Denn Mädchen werden in vielen Ländern benachteiligt und haben nicht die gleichen Chancen wie Jungen. Der Tag ist für alle Mädchen weltweit, also auch für die Mädchen in Deutschland. Foto: Plan International - ACHTUNG: Nur zur redaktionellen Verwendung und nur mit Nennung der Quelle: «Plan International» +++(c) dpa - Bildfunk+++
'Yan makaranta a NijarHoto: picture-alliance/dpa/Plan International

Nawani Aboki dai na zaman jagoran wasu kungiyoyin kusan dari biyar na masu zaman kansu. Ya ce: ''ana dai kallon shi kansa batun talauci da rashin tsaron da yai aure yake shirin tarewa a sashen arewacin ƙasar na da ruwa da tsaki da batun lalacewar ilimin a matakai daban- daban.''

Daga ƙasa za a iya sauraron rahoton da wakilinmu a Abuja Ubale Musa ya aiko mana a kan bayyanin da ƙungiyar ta yi, da rahoton wakilinmu na Mina Babangida Jibril da ke yin bita a kan rashin kulawar gwamnati, da Rahoton wakilinmu na Zinder Larwana Malam Hami dangane da yadda ake sayen jarabarwar a Nijar a ƙarshe da kuma rahoton Ibrahima Yakubu dangane da lalata da malamai ke yi da 'yan mata a manyan makarantu.

Mawallafi : Ubale Musa
Edita : Abdourahamane Hassane

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani

Nuna karin labarai