1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jagorar yankin Hong Kong ta fidda sanarwar gaggawa

Zulaiha Abubakar
September 3, 2019

Jagorar yankin Hong Kong ta sanar da cewar ita da mataimakanta za su kawo karshen rikicin da yankin ya tsunduma, bayan fitar wani sauti a kafafen sadarwar zamani dauke da muryarta tana bayyana shirin sauka daga mulkin.

https://p.dw.com/p/3Owvy
Hongkong Regierungschefin Carrie Lam
Hoto: picture-alliance/dpa/L. Hanxin

Da take kare kare kanta gwamnatin Chaina ta bakin kakakinta Xu Luying ta tabbatar da cewar kasar ta shirya tsaf don daukar matakin magance rikicin siyasar da ya tasamma ruguza yankin na Hong Kong, kodayake kasashe da dama sun zargi mahukuntan Chaina da hannu cikin wannan rikici a baya. Wani rukunin na 'yan kasuwa daga cikin masu zanga-zangar a Hong Kong sun zargi jagora Lam da yaudara, bayan daliban jami'a sun dauki matakin dakatar da zuwa makaranta har na tsawon makwanni biyu .

Yanzu haka 'yan Sandan yankin na tsare da mutanen da yawansu ya kai dubu 1,100 wadanda suka hada da yan siyasa tun daga watan Yunin da ya gabata.