1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD ta ce ana neman taimako gaggawa

Binta Aliyu Zurmi
December 2, 2021

Majalisar Dinkin Duniya ta ce bukatar agajin gagawa ta yi karuwar da ba a taba gani ba. A cewar hukumar OCHA sama da dalar Amirka bilyan 40 ake bukata a shekara mai zuwa.

https://p.dw.com/p/43ion
BG Photos and testimonies from Syrian photographers |  Omar Sanadiki
Hoto: Omar Sanadiki/OCHA

Hukumar bada agaji ta Majalisar Dinkin Duniya OCHA ta ce bukatar bada agajin gagawa ta yi karuwar da ba a taba ganin irinta ba, a sabili da annobar da duniya ke fuskanta a yanzu haka da ma matsalar sauyin yanayi da kuma tashe-tashen hankula a wasu kasashen da ke kara raba mutane da matsugunansu.

Hukumar ta OCHA ta ce akalla an yi kiyasin mutane miliyan 274 ne za su bukaci taimakon gagawa a shekarar da ke tafe. Wato karin kashi 17 cikin dari na mutanen da ake da su a yanzu haka, a cewar babban jami'in hukumar agajin.

A duk shekara sama da dalar Amirka biliyan 35 ake kashewa a kan masu bukatar agaji, sai dai saboda karin da hukumar ta ce za a samu, shekarar 2022 sai an  bukaci sama da biliyan 40 idan aka yi la'akari da halin matsin da al'umma ke ciki a kasashen  Habasha da Afghanistan da Myanmar da sauran wasu da dama.

A shekarar da ta gabata sama da mutum miliyan dari ne hukumar agaji ta OCHA ta kai wa dauki.