1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta ce ba ta tsaigaita wuta ba

July 13, 2013

Jagoran ƙungiyar Jama'atu Ahlis-Sunnah Lidda'awati Wal Jihad wato Boko Haram Imam Abubakar Shekau , ya fito fili ya karyata duk wani shiri na tattaunawa tare da gwamnatin Najeriya.

https://p.dw.com/p/197JB
This image taken from video posted by Boko Haram sympathizers shows the leader of the radical Islamist sect Imam Abubakar Shekau made available Wednesday Jan. 10, 2012. The video of Imam Abubakar Shekau cements his leadership in the sect known as Boko Haram. Analysts and diplomats say the sect has fractured over time, with a splinter group responsible for the majority of the assassinations and bombings carried out in its name. (AP Photo) THE ASSOCIATED PRESS CANNOT INDEPENDENTLY VERIFY THE CONTENT, DATE, LOCATION OR AUTHENTICITY OF THIS MATERIAL
Hoto: AP

Ƙungiyar ta ce ta  goyi bayan harin da aka kai a wata makaranta da ke a garin Mamudo a jihar Yobe wanda ke a yankin arewa maso gashin ƙasar, amma kuma ba tare da ɗaukar alhakin kai harin ba.

A cikin wani sabon sako na faifayin Bidiyo da ƙungiyar ta fitar, ta ce ba ta kai hari a kan 'yan makaranta. Yan makaranta kusan 42 suka mutu a harin da aka kai da makamai a farkon wannan wata a garin  na Mamudo akan wata makaratar ta Sakandri.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita        : Saleh Umar Saleh