Boko haram ta ƙwace garin Buni Yadi
August 21, 2014Talla
wani kakakin gwamnan jihar Yoben Abulahi Gaidam ya shaidawa kamfanin dilanci labarai na Faransa AFP cewar babu wani sojin gwamnati ko ɗaya da ke a can a halin yanzu.
Shaidu waɗanda suka tsere daga garin sun ce mayaƙan na Ƙungiyar Boko Haram sun kafa sansanisu a wani gini gwamnatin inda suka kafa tuttarsu,sannan kuma suka ce 'yan ƙungiyar sun kwashi ganima a cikin shaguna.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe