1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron kasuwancin Afirka da Birtaniya

Zulaiha Abubakar
January 20, 2020

Firaminista Boris Johnson na Birtaniya zai jagoranci wani taron kasuwanci tare da shugabannin kasashen Afirka 16, mako biyu gabanin kammala ficewar kasar daga kungiyar EU.

https://p.dw.com/p/3WSOB
UK - Africa Investment Summit 2020
Hoto: Reuters/B. Stansall

Wannan dai shi ne karo na farko da za a gudanar da taron kasuwanci da habaka tattalin arziki tsakanin Birtaniya da kasashen na Afirka.Yayin taron ana sa ran Firaminista Boris Johnson zai bayar da muhimmanci wajen jan hankalin 'yan kasuwa da masu masana'antu a Afirka, su zuba jari a Birtaniya da zarar ta kammala ficewa daga kungiyar Tarayyar Turai EU.

Daga cikin shugabannin kasashen Afirkan da zasu halarci taron, akwai shugaba Muhammadu Buhari na Tarayyar Najeriya da takwarorinsa na kasashen Masar da Kenya da kuma Ghana.