Birtaniya: Boris Johnson ya yi murabus
July 9, 2018Talla
Sakataren harkokin wajen Birtaniya Boris Johnson ya yi murabus kamar yadda bayanai ke fita daga Downing Street suka nunar. Wannan dai na nuni da cewa Firaminista Theresa May za ta samu kai a halin tsaka mai wuya kan yadda za ta tafiyar da harkokin mulkin kasar ta Birtaniya. Hakan dai na zuwa ne bayan ajiye mukami da mai shiga tsakani kan batun fitar Birtaniya daga Kungiyar EU David Davis ya yi ranar Lahadi.