Bemba ya yi watsi da sakamakon zaɓen ƙasar Kwango.
November 16, 2006Ɗan takara a zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasar Jumhuriyar Dimukraɗiyya Ta Kwango, Jean-Pierre Bemba, wanda ya sha kaye a zaɓen, ya yi watsi da sakamakon da hukumar zaɓen ƙasar mai zaman kanta, ta bayar jiya, inda ta ce shugaba mai ci yanzu Joseph Kabila ne ya lashe zaɓen.
Da yake jawabi a kan wata tasahar talabijin mai zaman kanta da yake mallaka, Jean-Pierre Bemba, tsohon shugaban ’yan tawaye, wanda kuma shi ne mataimakin shugaban ƙasa a gwamnatin riƙon ƙwaryar da ta yi mulki a ƙasar kafin zaɓen ya bayyana cewa, yana nadamar sanar da jama’an ƙasar da kuma al’umman gamayyar ƙasa da ƙasa, ƙin amincewarsa da sakamakon zaɓen, saboda a nasa ganin, bai dace da ainihin ƙuri’un da aka ka da ba.
Bemba dai ya ce zai yi amfani ne da duk hanyoyin shari’a wajen ƙalubalantar sakamakon.