1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yuyuwar barkewar rikici a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

Salissou Boukari
October 27, 2018

Tsohuwar kungiyar mayaka ta Seleka a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, ta bai wa wakilan gwamnatin kasar wa'adi na kwanaki biyu na su fice daga yankunan da ke karkashin kulawarta.

https://p.dw.com/p/37H1c
Zentralafrikanische Republik | Naturschutz in Krisengebieten | Soldaten vor dem Präsidentenpalast in Bangui
Hoto: Getty Images/AFP/S. Kambou

Jagoran tsofuwar kungiyar ta Seleka ne dai Abdoulaye Hissene, ya sanar da hakan a ranar Asabar, kwana daya bayan da 'yan majalisar dokokin kasar suka sauke shugban majalisar dokokin kasar Karim Meckassoua wanda Musulmi ne daga mazabar gunduma ta uku ta Bangui babban birnin kasar. Da yammacin ranar Juma'a ne dai 'yan majalisar suka sauke shugaban nasu, amma kuma a cewar Abdoulaye Hissene na kungiyar ta Seleka, sauke Meckassoua ba a yi shi a kan ka'ida ba, kuma an yi shi ne domin matsayinsa na Musulmi.

A baya dai an kalli zaben shugaban majalisar Karim Meckassoua a matasyin wani mataki na sulhu tsakanin 'yan kasar, ganin cewa shugaban kasar Faustin-Archange Touadéra na a matsayin Kirista.