Kalaman batanci ga Annabi ya haifar da rikici
October 20, 2019Talla
Kakakin 'yan sanda yankin Mohaiminul Islama ya ce, biyu sun mutu a yayin zanga-zangar yayin da sauran da aka ruga dasu asibiti suka mutu a gadon asibitin. Jami'an 'yan sanda sun yi amfani da barkonon tsohuwa wajen kwantar da tarzomar bayan da rikicin ya ki cinyewa.
Hargitsin ya soma ne bayan da aka gano yadda wani mabiya addinin Hindu, ya soki Annabin tsiran da 'yarsa Nana Fatima a rubutun da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Asabar da ta gabata. Koda 'yan sanda suka kama wanda ake zargin, ya musanta zargin inda ya ce, kutse aka yi wa shafin nasa.