1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Austriya: Za a kafa sabuwar gwamnati

Abdourahamane Hassane
December 16, 2017

Jam'iyyar masu ra'ayin rikau a Austriya tare da jam'iyyar masu kyamar baki sun gabatar da yarjejeniyar da suka cimma ta kafa gwamnati ga shugaban kasar Alexander Van der Bellen.

https://p.dw.com/p/2pUBf
Österreich Koalitionsverhandlungen ÖVP und FPÖ Strache und Kurz
Hoto: Reuters/L. Foeger

Sebastian Kurz ministan harkokin waje wanda jam'iyyarsa ta ÖVP ta samu nasara a zaben 'yan majalisun dokoki a watan Oktoba. Ya bude shawarwari da jam'iyyar masu kyamar baki ta FPÖ ta Heinz Christian Strache don samun rinjaye don kafa gwamnati. A shekara ta 2000 kungiyar tarrayar Turai ta sakawa Austriya takunkumin karya tattalin arziki bayan da jam'iyyar masu kyamar bakin ta shiga gwamnati.