1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gogayya tsakanin Amirka da Rasha kan Afirka

Abdourahamane Hassane
July 29, 2022

Ma'aikatar harkokin wajen Amirka ta ce jagoran diflomasiyyar Amirkar zai kai ziyara a cikin kasashen Afirka ta Kudu,da Jamhuriyar Dimukaradiyyar Kwango da Ruwanda,a cikin watan Agusta da ke shirin kamawa.

https://p.dw.com/p/4EtNO
Antony Blinken
Hoto: OLIVIER DOULIERY/AFP

Antony Blinken zai yi rangandi ne a wani yunkuri na dakile fafutikar da Rasha take yi na samun goyon baya a nahiyar Afrika, da kuma nuna muhimmanci hulda da Afrika. An shirya Jakadiyar Amirka a Majalisar Dinkin Duniya, Linda Thomas-Greenfield, za ta ziyarci kasashen Ghana da Uganda a wata mai zuwa, bayan da darektan hukumar ba da agaji ta Amirka Samantha Power ta kammala ziyarar da ta kai a Kenya. Yunkurin diflomasiyya na Amirka na zuwa ne a daidai lokacin da ministan harkokin wajen Rasha Sergey Lavrov ya fara rangadin a cikin wasu kasashen Afirkan,inda ya dora laifin hauhawar farashin kayan abinci a kan takunkumin da kasashen yamma suka kakabama kasarsa, furcin da Amirka ta yi watsi da shi.