1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ansaru ta hallaka 'yan kasashen ketare da ta yi garkuwa da su a Najeriya

March 10, 2013

Gwamnatocin kasashen Italiya da Birtaniya sun tabbatar da kashe 'yan kasashensu a yankin arewacin Tarayyar Najeriya.

https://p.dw.com/p/17ufV
A man reads a local newspapers with the headline 'We've killed 7 foreign hostages' on a street in Kano, Nigeria, Sunday, March. 10, 2013. The United Kingdom's military says its warplanes recently spotted in Nigeria's capital city were there to move soldiers to aid the French intervention in Mali, not to rescue kidnapped foreign hostages. The Ministry of Defense said Sunday that the planes had ferried Nigerian troops and equipment to Bamako, Mali. An Islamic extremist group in Nigeria called Ansaru partially blamed the presence of those planes as an excuse for claiming Saturday that it killed seven foreign hostages it had taken. ( AP Photo/Sunday Alamba)
Hoto: picture alliance/AP Photo

Gwamnatocin kasashen Italiya da Birtaniya sun tabbatar da kashe 'yan kasashen, da ke cikin wadanda wata kungiya ta yi garkuwa da su, a yankin arewacin Tarayyar Najeriya, a watan da ya gabata.

Mutanen bakwai da aka hallaka bayan garkuwa da su, sun hada da 'yan kasashen: Birtaniya, Italiya, Girka da Lebanon. Kungiyar ta Ansaru mai da'awa da sunan addinin Islama, ita ce ta bayyana kisan bayan garkuwa da mutanen.

Ministan harkokin wajen Birtaniya William Hague cikin wata sanarwa ya ce, akwai yiwuwar cewa an hallaka mutanen bayan garkuwan. Firaministan Italiya Mario Monti ya ce gwamnatin kasar za yi duk abun da ya dace, domin gurfanar da masu garkuwan a gaban kotu.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Yahouza Sadissou Madobi