An zargi sojojin Mali da kisan farar hula
August 10, 2018Talla
Bincike ya nunar da cewa so uku sojoji suna kai hari ba tare da yin la'akari da rayuwar fararen hula ba. An gano yadda mutum goma sha biyu suka rasa rayukansu a wani hari da sojin suka kai a wata kasuwar shanu dama wasu wurare biyu. Majalisar ta bayyana damuwa kan kisan da ta ce laifi ne da ya keta hakkin bil Adama.
Gwamnatin Mali dia a farko ta daura alhakin kisan kan mayakan jihadi, daga baya ta amince da laifin bayan da aka gano wasu kabura da aka binne gawarwakin mutane, ta kuma ce ta soma na ta binciken kan wannan ta'asa.