1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Mali: Kinsan 'yan ta'adda ya bar baya da kura

Abdoulaye Mamane Amadou
April 6, 2022

Wani rahoton kungiyar kare hakin bil Adama ta Human Rights Watch ya zargi sojan Mali da kisan fararen hula akalla 300 bisa tuhumarsu da zama 'yan ta'adda a yankin Mura na kasar.

https://p.dw.com/p/49WJT
Afrika Militär Missionen von Barkhane in Mali
Hoto: Etat-major des armées / France

Kungiyar Human Rights Watch ta ce abubuwan da suka faru a Mura na zama mafi muni tun bayan barkewar rikici a kasar Mali a shekarar 2012, a yayin da ta tattara shedu 19 da suka hakikance kisan fararaen hula a yankin da sunan 'yan ta'adda.

A yanzu ya zama wajibi a cikin gaggawa hukumomin mulkin soja a Mali da su kaddamar da binicke na hadin gwiwa da kungiyoyin kasa da kasa kan zarge-zargen taka hakin bil'Adama, a cewar Corinne Dufka daraktar kungiyar Human Rights Watch a yankin Sahel.

Sai dai da ta ke mayar da martani a cikin wata sanarwar da ta fitar rundfunar tsaron kasar Mali ta yi fatali da zarge-zargen da ake yi mata, tana mai cewar wani yunkuri ne kawai na shafa mata kashin kaji.