1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An zantar da hukuncin kisa a Afganistan

November 22, 2012

Hukumomin Afganistan sun rataye mutane shidda da a ke zargi da cin amanar ƙasa

https://p.dw.com/p/16nlX
Rope © Mykola Velychko #4398733
Igiyar rataye mutaneHoto: Fotolia/Mykola Velychko

Hukumomin Afghanistan, sun aiwatar wa wasu mutane shidda hukuncin kisa ta hanyar ratayewa a wannan Larabar. Ministan harkokin shari'ar kasar ne ya bayana sanarwar kashe mutanen jim kadan bayan da aka zartar da hukuncin. An tuhumi mutanen ne da laifin cin amanar kasa bayan da aka same su da hannu a hare haren da suka yi sanadiyar mutuwar a kalla mutane 45, a jerin hare haren da suka kai a birnin Kabul na kasar a shekara ta 2010. Jim kadan kafin zartar da hukuncin, shugabannin Taliban sun yi barazanar daukar fansan mutanensu, indan har aka aiwatar musu da hukuncin na kisa. Kimanin mutane 14 ne aka rataye tun farkon wannan shekarar a kasar ta Afghanistan.

Mawallafi: Issoufou Mamane

Edita: Usman Shehu Usman