1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An soma binciken Shugaba Ramaphosa

Gazali Abdou Tasawa
June 12, 2019

Wata mai shari'a a Afirka ta Kudu ta soma gudanar da wani bincike kan shugaban kasar Cyril Ramaphosa dangane da wata badakalar cin hanci da ake zargi da hannunsa a ciki. 

https://p.dw.com/p/3KF0f
Südafrika Präsident Cyril Ramaphosa in Pretoria
Hoto: AFP/P. Magakoe

Wata mai shari'a mai zaman kanta ta kasar ta Afirka ta Kudu Busisiwe Mkhwebane wacce aka dora wa nauyin sa ido kan yadda gwamnatin zartarwa ke tafiyar da ayyukanta ita ce ta sanar da bude binciken kan batun wasu kudaden gudunmawar yakin neman zabe da wani kamfani ya zuba wa shugaban kasar a lokacin yakin neman zabensa.

 A baya dai shugaba Ramaphosa ya kare kansa yana mai cewa tallafin kudin Euro dubu 30 da kamfanin Bosasa ya bayar, ya ba da shi ne ga dansa Andile mai bayar da shawara ga kamfanin. 

Mai shari'ar na zargin taka wasu dokoki na da'ar aiki da aka shinfidawa mambobin gwamnati. Shugaba Ramaphosa wanda ke kan karagar mulkin kasar yau shekara daya da rabi ya sha alwashin kawar da matsalar cin hanci da ta dabaibaye kasar da ma ta kasance dalilin tsige Shugaba Jacob Zuma daga kan mukaminsa.