1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matasa sun ki amsa kiran hukumar zaben Tunisiya

Zulaiha Abubakar
September 15, 2019

Hukumar zaben Tunisiya ta ce ba ta ji dadin yadda jama'a da dama suka ki fita don ka'da kuri'u a zaben shugaban kasa da aka gudanar a wannan Lahadin duk kuwa da kiraye-kirayen da shugabanta ya yi musamman ga matasa.

https://p.dw.com/p/3Pe29
Präsidentenwahl in Tunesien
Hoto: Picture-alliance/AP Photo/H. Dridi

Gabannin zaben dai al'ummar kasar sun bukaci sabon shugabancin da za a samu ya magance matsalar karyewar tattalin arziki da kuma rashin aiki tsakanin matasa. Kafin wannan lokaci dai da dama daga cikin al'ummar kasar na yi wa Nabil Karoui guda daga cikin attajiran kasar kyakkyawan zaton zai fitar musu da kitse daga wuta duk kuwa da cewar gwamnati ta zarge shi da  musayar kudade ba bisa ka'ida ba.