An sace ma'aikatan Red Cross a Afghanistan
August 16, 2014Talla
Ƙungiyar ta Red Cross ta ce lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da ta gabata a sa'ilin da tawagar ma'aikatan ke kan hanyarta ta zuwa garin Herat a cikin mota.
A jiya jumma'a ma kafofin yaɗa labarai na ƙasar sun rawaito cewar 'yan Taliban sun sace wasu jami'an masu aikin cire nakiyoyi a garin Ghazni da ke a yankin yammaci. Hukumomin tsaro na ƙasar ta Afghanistan sun gargaɗi baƙi da su riƙa sanar da su tafiye-tafiyensu.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Zeinab Mohammed Abubakar