Matsin lamba ya janyo nadin gwamnati a Mali
September 21, 2020Talla
Biyo bayan matsin lamba daga kasashe makwabta da kungiyar habbaka tattalin arzikin yammacin Afrika ta ECOWAS ko CEDEO, sojojin da suka jagoranci juyin mulki a Mali sun bayar da sanarwar kafa gwamnatin rikon kwarya a kasar.
Dama can shugabannin kasashen yammacin Afrika sun jajirce lallai sai an kafa gwamnatin rikon kwarya ta farar hula da zata sake maida madafun iko ga hannun wata zababbar gwamnati cikin watanni 18, ko da kuwa mataimaki zai kasance daga bangaren 'yan juyin mulkin inda Kanal Assimi Goita ya kasnce mai taimakawa sabuwar gwamnatin.