Abiy Ahmed na neman hadin kan al'umma
June 16, 2021Talla
Aby Ahmed da ke magana a Jimma mahaifarsa da ke a yankin Oromia a arewacin kasar a farfagandinsa a rana ta karshe ta kampe kafin zaben 'yan majalisar dokokin da za a yi a ranar 21 ga watan Yuni(21-06-21), ya ce yin haka shi ne wajibi. Zaben na 'yan majalisun dokoki wanda aka shirya yi tun a cikin watan Augusta na shekara ta 2020 an dageshi har' sau biyu saboda corona abin da ya janyo tayar da kayar baya na 'yan yankin Tigray da suka nemi balewa.